❣🤦🏻♂ _*KUSKURENA*_❣🤦🏻♀
{The story is Interesting! Attractive! Impressive! to cut a long story short the story is a fascinating story the readers will entertain and enjoy it.}
❣❣❣❣❣❣❣❣❣❣❣
**************************************
❣❣❣❣❣❣❣❣❣❣❣
*BY*
_*©, RAMLERT Y SALIS*_
~08037862213✍🏻~
*No part of this book maybe an object of privacy✖*
_Thurs , October 17 , 2019._
_*Page 18......*_
Sai daya dau kamar mintuna 15 hk yana ta ajiyar zuciya Sannan ya umarci nurses din dake tsaye a kansa dasu kawo masu wasu abubu daya bukata babu 6ata lokaci suka kawo masa.
Tana kwance a hankali abubuwan dasuka faru tsakaninta da Safraz suka fara dawomata cikin Brain dinta hawayene suka fara rolling dg eyes dinta, meyafaru? Shine abinda take ta tambayar kanta duk da batasan menene dalilin dayasa Safraz yayi Mata hk ba amma is a serious problem jitayi kawai she's eager to know what happened a hankali take yunkurin tashi zaune da sauri doctor Mahmud ya iso bakin gadon ya dakatar da ita.
Idonta dasuke a kumbure ta daga ta kalli doctor in a lower voice tace, Pls I want to see my husband, takarasa mgnr wasu guntun hawaye na fitowa from her eyes.
Da mamaki doctor Mahmud yayi saurin Kallonta daga masa Kai tayi cikin kulawa yace, Calm down !!! You will see him later but not now sorry.
Yana gama fadin hk ya kalli nurses din yafice a dakin, daf da ita suka karaso suka fara kokarin sakamata wata doguwar Riga me kama da rigan sanyi bayan sunsa mata daya dg cikinsu ta mika Mata cup dauke da tea mai kauri babu gardama Izzatu ta karba ta fara sha sai data sha fin rabi cup din Sannan ta mika musu, kamar mintuna biyar takuma bata wani cup din me dauke da warn water Izzatu ta karba, Magani ta dinga bata tana sha har ta gama Sannan ta koma ta kwanta suka wanke mata ciwon dake goshinta tare da daura mata ruwa Sannan suma suka Fice babu bata lokaci itama bacci ya dauketa.
Office dinsa yakuma kaisu bayan sun zauna doctor Mahmud ya kallesu muryansa a sanyaye yace, ina me Neman afuwarku bisa kuskuren Dana aikata na tayar muku da hankali wallahi lokacin da aka kawota nayi duk iya bincikena alamu suka nunamin ta rasu amma Ashe akasin hkne yau muna daukota da zummar Baku ita kawai sai na lura kamar tana hiccup cikin izinin Allah gashi har ta farfado, Ashe tayi long faint ne.
_Alhamdulillah! Alhamdulillah Alhamdulillah_ shine abinda Alhaji Hashim yake ta maimaitawa , Prof kuma ya sunkuyar da kansa kasa sai ga wasu hawaye masu dumi sun zubo masa.
Basu wani bata lokaci ba doctor ya kaisu har dakin suka ganta tanata barcinta cikin kwanciyar hankali.kafin kace me tuni labarin farfadowar izzatu ya yada family masu tahowa asibitin nayi masu kukan farinciki ma nayi hkm masu bakinciki nayi, lokacin da labarin ya isarwa su Anty Adama sai datayi kamar ta hadiyi zuciya ta mutu saboda bakin ciki abangaren karima ma hkne ranta yayi mugun baci har sai data kasa dannewa ya bayyana akan fuskarta.
Wajen karfe daya Izzatu ta farka dg bacci, lokaci yan dubiya suka samu damar shigowa dakin cika yayi da mutane anatayi mata sannu Hajiya Rukayya bakin ta yaki rufuwa domin ganin tilon diyar tata ta bude ido kamar an mata kyautar aljanna hk takeji.
Tunda yanxu Alhamdulillah ga yadda ta kasance kabada izini asaki Safraz, Prof ya fada yana kallon Alhaji Hashim.
Hmmm Rabu dashi sai na koya masa darasi tukunna nan gaba bazai kara Kuskuren kai hannu kan matarsa ba, cewar Alhaji Hashim.
A"a Alhaji ba hk za ayiba hakuri za,ayi ansan yayi *Kuskure* sai ayimasa afuwa Allah yanason masu yafiya domin Sam ba halinsa bane.
Jafar dayake zaune agefe yace, Abba Dan Allah kayi hakuri sharrin shaidanne amma suna zamansu lpy Dan Allah Abba ayi masa afuwa in sha Allah wannan shine na farko kuma na karshe.
Alhaji Hashim yaji dadin yadda prof yake nuna kulawa ga dansa Safraz shikanshi kwana yayi baiyi bacci saboda damuwar abinda dayayiwa Safraz din sam bayason damuwar dan nasa ko kadan Amma girman laifin daya aikata bazaisa yaki hukuntasa ba.
Da kyar suka samu ya yarda, yan sanda ya kira yace in anzo bailing Safraz subada shi.
Babu bata lokaci Prof da jafar sukaje suka karboshi kasan cewar ko takalmi babu a kafarsa yasa Prof yasa jafar ya tsaya a wata plaza yafita ya sayi takalmi da set din kayan da zaiyiwa Safraz basu tsaya ko inaba sai wani Dan karamin hotel Prof ya umarci Safraz yaje yayi wanka ya bashi kayan daya siya, Babu musu Safraz ya karba ya Shiga duk tunaninsa wajen zana izar Izzatu zasu, dg jafar har Prof duk tausayinsa ya cikasu Dan jikinsa yayi rudu rudu alamun yasha duka ga cizon sauro abunka da farin mutum fatarsa tayi ja duk ya kumbura.
Safraz ko daya shiga toilet din bai samu damar yin wanka ba kuka yayi har ya gode Allah ya wanke fuskarsa kawai ya canza kaya ya fito suka tafi.
Koda sukazo asibitin Safraz bai kawo komai aransaba suna tafe yana binsu har dakin da Izzatu take, zuwa lokacin babu mutane sosai a dakin dg mami sai Hajiya Rukayya da Hafsa matar jafar sai sakina da Alhaji Hashim.
Prof ne ya fara shigowa sai jafar saikuma Safraz yana biye a baya, yana shigowa Izzatu dake zaune takai kallonta kanshi wani bala,in tausayinsane ya bugi zuciyar ta Dan duk Hafsa ta fadamata abun daya faru na kowa yayi zaton ta mutu da dalilin dayasa Safraz ya daketa dakuma yan sanda da babansa yasa suka kamashi, har text din saida hafsa ta bata ta karanta domin da safe jafar yaje gidan ya gyara inda ya baci da jini da glass cup din daya tarwatse nan ya dauko wayoyin Izzatu da Safraz ya bawa Hafsa ta ajiye.
Shima Safraz kurawa izzatu ido yayi yana tunanin kodai mafarki yakeyi ne Amma ganin zahirin gaskiya ne ba mafarki ba yasa ya karasa bakin gadon da sauri, kallon juna suka dinga yi hawaye nabin fuskokinsu bawanda ya iya cewa wani Abu.
Alhamdulillah ya furta yanayin murmushi da hawaye nakuma bin fuskarsa zama yayi abikin gadon yana ta dariya shi daya kamar mahaukaci, Alhaji Hashim ne yace, dariyan me kakeyiwa mutane da kana Santa kayimata hk idan Bacin akwai sauran kwannan a nan gaba da tuni shikenan To wallahi inayimaka last warning kar inkara ganin makamancin hk kuma yanxu ka tsugunna ka bata hakuri.
Safraz da kansa yake a sunkuye a hankali ya tsugunna har kasa ya kalli Izzatu yace, ina Neman afuwarki Dan Allah kiyi hakuri.
Duka dakin sai dayabawa kowa tausayi Izzatu kam fashewa tayi da kuka.
Kwanan Izzatu biyu a asibitin aka sallameta, taso ta wuce gidansu Amma mahaifinta ya hana dole takoma gidan ta, Ranar juma ,a bayan anyi sallar juma,a aka daura auren Safraz da karima a inda Prof shine waliyin Safraz wani kanin mahaifin karima yazama mata waliyinta, farinciki wajen Karima babu iyaka domin samun cikar burinta Wanda ta kudurce a zuciyar ta muddin tashiga gidan Safraz sai tayi mai yiwuwa Dan fitar da Izzatu koda kuwa ta hanyar bin malsmai ne. Safraz kuwa babu yabo babu fallasa bazakace yana farinciki ba hkm bazskace tana bakinciki ba, damuwarsa duk yana kan Izzatu kullum kara jin Santa yakeyi a zuciyarsa Amma abinda yafaru Sam yayi masa Katanga da ita Dan ko mgn ba sosai Sukeyiba, Izzatu kuwa ta murmure Masha Allah duk da tana cikin damuwa Amma tabarwa Allah lamarunta tunanin ta bai wuce halin dazata Shiga idan karima ta shigoba babu abinda yake hadata da Safraz gashi ya kara aure hk zata dinga Kallonsa shida matarsa ita kuma tana gefe wannan shine abinda yafi damunta.
Ajiyar zuciya Izzatu tayi ta kalli Ramlert da Dan guntun hawayen dake idonta ya karasa fitowa Sannan tace, Ramlert this is end of my story Amma na yakaice miki labarinne because there's no enough time.
Tabbas you're Best among the rest kawata I pity you I can not define describe how I feel, sorry Izzatu be patient kikara hakuri sosai Amma nima ina cikin rudani me tarin yawa Allah ya tona musu asirin kasuwaye, karki dami zuciyarki da tunane-tunane akan wannan auren take it easy don't bother yourself keep praying Allah zai ganar dashi watarana. Cewar Ramlert.
Hmmmm Ramlert kenan nasan dole zan wulaqanta idan matarsa ta shigo yanxu ma baya tani inaga yasamu wata, Duk wani abunda kikaga yafaru a wajen dinner dinnan yanata wani haba-haba dani duk yayi ne Dan kar a gane har yanxu akwai matsala a tsakaninmu Dan na Dade banga yayi dariya kamar irin ta ranar ba na fahimci bayason karima ta gane akwai wata matsalar a tsakaninmu, ina San Safraz matukar so Amma zan iya hakura dashi matukar nafuskanci wani wulakanci idan matarsa ta tare.
No Izzatu karkice hk matsalar dayane wannan tsargin dake tsskaninku Amma wallahi he loves u More than u love him, every a bad beginning has a good ending take patient akwai ranar dazai fahimta gaskiya Zata bayyana, da safe baya miki so mai tsanani da tuni ya sakeki Amma he can't separate with you because he loves you so much ni dai shawara gareki ki kara hakuri inhar abun yaki to sai asan yadda za,ayi inta kama arabu din Amma indai kika matsa kuka rabu yanxu babu wani nasara domin har abada bazai daina zargin abinda kikayi masa Amma yanxu inkuna tare maybe the true will appear, ki kara juriya da hakuri me hakuri na dafa dutse har yasha romonsa.
Izzatu tace, thank for your advice my dear may Allah reward you Amply, Allah ya barmu tare my sister good friend like no another.
Sun Dade sun tattaunawa Sannan Writer Ramlert ta tafi.
A can gidan mami kuwa cike yake da jama'a anata hidima domin duk a gidan aka hade bikin karima da Safraz din, dan babansu Karima ma wani bangare aka basu acikin gidan abata gudanar da biki cikin kwanciyar hankali.
Amarya tana ta doki saboda gobe za,a kaita dakin ta tasha gyara sai walkiya takeyi fauza babbar kawar amarya suna like da juna anata gudanar da shagali, Sakina kuwa bayabo ba fallsa tana Dan nuna farin ciki Amma damuwace fal zuciyar ta. Ango Safraz kuwa yana can gidansa tamkar ba Ango ba domin tun safe yana daki a kwance yanata tunane tunansa karima kuwa ganin bata ganshiba gashi wasu friends dinta nason su gaisa dashi yasa tadamesa da kira tsaki yaja a ransa yace " _malama don't bother me now bakya gabana damuwar datake gabana ma ta isheni, haka kawai a mannamin wahala_" yakuma gyara kwanciyarsa yaja blanket ya rufa.
~Sannu sannu kwane nesa muje zuwa page 19 yau da gobe bata bar komai ba~
0 comments:
Post a Comment